fidelitybank

Kusan Malam makaranta 4,000 sun faɗi a jarabawa

Date:

Hukumar yi wa Malaman Makaranta Rijista ta Najeriya (TRCN) ta bayyana cewa kimanin malaman makaranta dubu uku da dari tara da sittin da uku ne suka faɗi jarrabawar da ke nuna ƙwarewa da suka zana a watan Nuwamban wannan shekara ta 2023.

Hukumar ta ce malamai dubu goma sha biyar da dari bakwai da hamsin da uku ne suka zauna jarabawar, daga ciki dubu goma da dari shida da talatin da shida suka samu nasara, yayin da dubu uku da dari tara da sittin da uku suka fadi.

Wannan lamari ya sa masana a ɓangaren ilmi a Najeriya yin tsokaci game da batun.

Masana irin su Dakta Aliyu Umar Tilde, tsohon kwamishinan ilimi na jihar Bauchi, ya ce jarabawa ce mai kyau saboda “da yawa daga cikin malamai, ana samu suma kansu suna buƙatar karatu.”

Ya ba da misali da jihar Kaduna inda a kwanakin baya, aka yi wa malamai jarabawa kuma da yawan su suka faɗi.

“Sanin cewa akwai rauni wajen horar da malaman shi ne ya sa dole a samar da jarabawa kafin a ba da lasisi”, kamar yadda masanin ya ce.

Ya ce a baya, ba a irin wannan jarabawa ta tantance ƙwarewar malami saboda karatu a lokacin yana da ƙarfi a makarantu “amma daga baya da makarantu suka yi yawa, har da na jeka na yi ka, akwai kuma yaudara da shaidar karatu ta bogi, wannan shi ne ya tilasta cewa ya kamata a jarraba ka kafin a tabbatar.” in ji Dakta Tilde.

Ya bayyana cewa akwai buƙatar a yi gyara sosai a ɓangaren ilimi na Najeriya idan ana son tsarin karatu ya koma irin na shekarun baya, lalacewar gwamnati shi ne ya haifar da lalacewar ilimin, a cewarsa.

Masanin ya ce sai an samu gyara ta ɓangaren gwamnati da su kansu malaman sannan al’amura za su daidaita a tsarin ilimin ƙasar.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp