fidelitybank

Kurunkus: Ganduje ya nuna wanda zai gaji kujerarsa a 2023

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya zaɓi mataimakinsa Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda zai gaje shi a babban zaɓe na 2023.

Wasu majiyoyi a fadar Gwamnatin Kano, sun shaida wa BBC Hausa cewa, an cimma matsayar ce yayin wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC mai mulkin Kano da aka gudanar a yau Asabar.

Sai dai wata majiya da ta nemi a ɓoye sunanta ta faɗa wa BBC Hausa cewa, har yanzu ba a kai ga daddale wannan zaɓi ba a hukumance.

Kazalika, an ruwaito cewa taron ya amince Kwamashinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu Murtala Sule Garo ya zama mataimakin Gawuna a takarar ta su.

Ana kallon matakin a matsayin wani sauyi daga goyon bayan da Murtala Garo ke samu na wasu jiga-jigan gwamnatin, ciki har da matar gwamna Hajiya Hafsat Ganduje, a matsayin wanda zai maye gurbin Ganduje.

Matakin na zuwa ne kwana biyu bayan Kotun Ƙoli ta tabbatar wa ɓangaren Ganduje shugabancin APC a Kano, sakamakon rikicin da ya biyo bayan zaɓukan shugabanci a watan Oktoba tsakaninsa da ɓangaren tsohon Gwamna Sanata Ibrahim Shekarau.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp