Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya zaɓi mataimakinsa Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda zai gaje shi a babban zaɓe na 2023.
Wasu majiyoyi a fadar Gwamnatin Kano, sun shaida wa BBC Hausa cewa, an cimma matsayar ce yayin wani taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC mai mulkin Kano da aka gudanar a yau Asabar.
Sai dai wata majiya da ta nemi a ɓoye sunanta ta faɗa wa BBC Hausa cewa, har yanzu ba a kai ga daddale wannan zaɓi ba a hukumance.
Kazalika, an ruwaito cewa taron ya amince Kwamashinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu Murtala Sule Garo ya zama mataimakin Gawuna a takarar ta su.
Ana kallon matakin a matsayin wani sauyi daga goyon bayan da Murtala Garo ke samu na wasu jiga-jigan gwamnatin, ciki har da matar gwamna Hajiya Hafsat Ganduje, a matsayin wanda zai maye gurbin Ganduje.
Matakin na zuwa ne kwana biyu bayan Kotun Ƙoli ta tabbatar wa ɓangaren Ganduje shugabancin APC a Kano, sakamakon rikicin da ya biyo bayan zaɓukan shugabanci a watan Oktoba tsakaninsa da ɓangaren tsohon Gwamna Sanata Ibrahim Shekarau.