Wani dandazon mata ya rufe kofar shiga Majalisar Dokokin ta kasa, saboda a cewarsu watsi da aka yi da bukatunsu jiya Talata a zauren Majalisar.
BBC ta rawaito cewa, a jiya ne ‘yan majalisar suka fara kuɗa ƙuri’a kan wasu ƙudirori da aka gabatar na gyaran kundin tsarin mulki, ciki har da wanda ya nemi a bai wa matan kashi 35 cikin 100 na muƙaman siyasa, amma sai ‘yan majalisar suka yi watsi da shi.
“Ba za mu bar wajen nan ba har sai mun ga shugaban majalisa, sai majalisa ta bai wa mata ‘yancinsu,” a cewar Niri Goyit daga ƙungiyar Action Aid.
Lamarin ya faru duk da cewa Matar Shugaban Ƙasa Aisha Buhari ta je majalisar da kanta a makon da ya gabata don gane wa idonta da kuma tabbatar da cewa ƙudirorin mata sun samu karɓuwa a gyaran kundin tsarin mulkin.
A yau Laraba ne ‘yan majalisar za su kammala kaɗa ƙuri’a kan batutuwa kusan 60 da suka shafi gyaran ɓangarori daban-daban na kundin mulkin.