fidelitybank

Kungiyoyin Kwadago a Kano da kasa na gudanar da zanga-zangar lumana

Date:

Gamayyar ƙungiyoyin ƙwadago na NLC ta TUC a Najeriya, sun fara gudanar da zanga-zanga ta ƙasa baki daya don nuna rashin amincewa da janye tallafin man fetur da gwamnatin kasar ta yi.

Shugabanni da mambobin ƙungiyar da dama sun taru a fitaccen dandalin ‘Unity Fountain’ da ke tsakiyar Abuja babban birnin ƙasar, riƙe da tutoci da allunan da ke ɗauke da saƙonni daban-daban.

Haka kuma rahotonni daga sassan ƙasar daban-daban sun nuna cewa tuni ƙungiyoyin suka fara gudanar da zanga-zangar a fadin jihohin ƙasar.

A jihar Kano da ke arewacin Najeriya wakilinmu ya ce ɗaruruwan mambobin ƙungiyar ne ciki har da mata suka fito domin gudanar da zanga-zangar

A ranar Litinin ne shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya yi wani jawabi ga ‘yan ƙasar, inda a ciki ya jajanta wa `yan al’ummar ƙasar dangane da halin matsi da matakin janye tallafin ya jefa su ciki, amma ya ce babu wani zabin da ya fi janye tallafin.

Sannan shugaban ya sanar da wadansu matakai da gwamnati ta ɗauka don rage raɗadin janye tallafin.

Sai dai kungiyar kwadagon ta ce babu wani tasiri da za su yi wajen rage wa al`umma ukuba.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp