Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu daga ƙungiyoyi 110 na neman yi musu rajistar zama jam’iyyar siyasa a ƙasar.
Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Laraba a Abuja, babban birnin ƙasar.
Farfesa Yakubu ya ce yanzu haka hukumar na nazarin buƙatun ƙungiyoyin bisa dokoki da ƙa’idojin da hukumar ta shimfiɗa.
“Ya zuwa yanzu mun tabbatar da samun waɗannan buƙatu, sai kuma wasu shida da suka aiko a baya-bayan nan da zuwa yanzu ba mu ba su takardar tabbatar da karɓar buƙatun nasu ba, kuma za mu ba su kafin ƙarshen makon da muke ciki”, in ji shi.
Shugaban hukumar ta INEC ya kuma buƙaci ƴan ƙasar, musamman waɗanda ke son rajistar zama jam’iyyar siyasa su riƙa tuntuɓar hukumar domin sanin ƙa’idojin yi wa jam’iyya rajista.