fidelitybank

Kungiyar Yarbawa ta yi tir da zaben Tinubu

Date:

Pa Ayo Adebanjo, shugaban kungiyar Yarabawa ta Afenifere, ya mayar da martani kan ayyana ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa.

Yayin da yake magana a wata tattaunawa ta wayar tarho da BBC, Adebanjo ya bayyana zaɓen da ya bai wa Tinubu nasara a matsayin mai cike da kura-kurai.

Ya ce sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma hakan na iya haifar rikici a ƙasar.

Adebanjo ya ce gazawar da INEC ta yi na amfani da na’urar BVAS a rumfunan zaɓe kamar yadda ta yi alkawari tun da farko, ya nuna cewa wasu sun tsara yadda zaɓen zai gudana da kuma ɗan takara da suke so ya yi nasara.

Ya ƙara da cewa a iya saninsa, shi dai ba a gudanar da zaɓe a ƙasar ba a ranar Asabar ɗin da ta gabata.

“Wannan ba zaɓe ba ne kuma duk mun san haka, a fili ta ke cewa an tafka maguɗi kuma hakan ba abin yarda ba ne.

“Hakan ba zai yiwu ba, su waye ke aika sakon taya murna ga zaɓabɓen shugaban ƙasa? Har yanzu ba mu gudanar da zaɓen shugaban ƙasa ba.”

Adebanjo ya bayyana cewa ba jam’iyyarsa ta siyasa ce kaɗai ta yi Allah-wadai da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba, har ma da masu sa-ido na cikin gida da na waje da suka shaida yadda zaɓen ya gudana da ma ɗaukacin jam’iyyun adawa ba su ji daɗin yadda zaɓen ya gudana ba.

Ya kuma yi nuni da cewa maguɗin zaɓe na iya jefa ƙasar cikin rikici kamar yadda wani tsohon shugaban ƙasar ya yi kira da a soke zaɓen.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp