fidelitybank

Kungiyar TNM za ta samar da mafita a 2023 – Kawu Sumaila

Date:

Tsohon mai bai wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari shawara kan al’amuran Majalisar Wakilai, Abdulrahman Kawu Sumaila, ya ce, sabuwar kungiyar siyasar nan ta TNM za ta sama wa ‘yan Najeriya mafita a 2023.

Kawu, wanda tsohon dan Majalisar Wakilai ne, ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya na cewa siyasar Najeriya na bukatar kungiya irin TNM.

Ya ce, “Ina goyon bayan wannan tafiya saboda za ta farfado da dimokuradiyya ta kuma samar da shugabanci na gari, ci gaba da sauran manyan nasarori”, inji shi.

Kazalika, Kawu ya ce, zai goyi bayan duk wata tafiya da za ta karfafa dimokuradiyya kafin babban zaben 2023, ba tare da la’akari da bambancin ra’ayin da ke tsakaninsa da wasu ba.

Tsohon dan majalisar ya kara da cewa wadanda suka kirkiri tafiyar ta TNM mutane ne da ke da tarihi da kwarewa a fagen siyasa.

“Wadanda suka kirkiri wannan tafiya ta TNM da tsarinta sun shirya sosai. Ina murna saboda yawancinsu suna da gogewa a harkar siyasa,” inji tsohon dan majalisar.

Aminiya ta rawaito cewa, masu sharhi a kan al’amuran siyasa dai na ganin zai yi wuya a samar da wata kungiyar siyasa a wannan lokacin har ta yi tasiri a zabukan 2023.

Ko gabanin zabukan 2019 ma wasu jigajigan ”yan siyasa sun yi yunkurin samar da wata tafiya da juya akalar siyasar Najeriya, amma daga karshe ba ta sake zane ba.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp