Ƙungiyar Tarayyar Turai ya bayar da tallafin dala 150,000, kwatankwacin naira miliyan 75 don yaƙi da yaɗuwar cutar mashaƙo a Najeriya.
Tare kuma da taimaka wa al’umomin da suka kamu a jihohin Kano da Katsina da Legas da kuma Osun.
Tarayyar Turan ta ce ta ɗauki matakin ne sakamakon ƙaruwar yaɗuwar cutar a Najeriya tun farkon shekarar 2023.
Za a bayar da tallafin ne ga mutane sama da miliyan daya da rabi, inda za a fi bayar da fifiko kan mutanen da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar.
Waɗanda ke zaune a wurare masu wahalar zuwa, kamar yadda ƙungiyar ta EU ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.
Tallafin wani ɓangare ne taimakon da ƙungiyar ke haɗawa na tara asusu don magance aukuwar bala’o’i a ƙasashen duniya ta hanyar ƙungiyoyin Red Cross da Red Crescent.