fidelitybank

Kungiyar Niger Delta ta yi tir da harin Edo

Date:

Kungiyar Niger Delta Congress (NDC), ta yi Allah wadai da harin ‘yan ta’adda a jihar Edo, tare da gargadin karuwar rashin tsaro a yankin.

Kungiyar ta fitar da wata sanarwa a ranar Talata a matsayin martani ga sace matafiya da dama a Igueben a ranar Asabar din da ta gabata.

Lamarin ya yi sanadin jikkata wasu fasinjoji tare da yin garkuwa da sama da 30 yayin da suke jiran hawa jirgin kasa daga tashar Igueben zuwa Warri a jihar Delta.

Kakakin NDC, Mudiaga Ogboru, ya yi Allah-wadai da harin kwanton bauna da aka yi wa ‘yan kasar da ba su ji ba ba su gani ba, inda suke lura da hare-haren da aka kai tun bara.

Ya ce “Harin ta’addanci iri daya da aka samu nasarar aiwatarwa a Igueben” an yi yunkurin kai shi ne a tashar jirgin kasa ta Abraka da ke Delta a ranar 8 ga Yuli 2022 da “yan ta’addar da suka yi kama da makiyaya”.

Kungiyar ta kuma tuno da munanan hare-haren da aka kai kan al’umomin Rivers, Bayelsa, da Cross River a watannin karshe na shekarar 2022.

Da yake lura da cewa yawan abin ya dame su, NDC ta ce duk da kiraye-kirayen da masu ruwa da tsaki da jama’a suka yi, gwamnonin ba su kafa jami’an tsaro na yankin ba a matsayin shaida na sadaukar da kai na tabbatar da tsaro da rayuka da dukiyoyi.

Hukumar ta ayyana “kishin su na daukar mataki”, duk da korafin da ake ci gaba da yi a yayin da rahotannin wasu mutane da ba a sani ba dauke da makamai ke fakewa a gandun dajin, “ya zama abin da ba zai yuwu ba kuma ba za a amince da shi ba”.

NDC ta bukaci gwamnonin yankin da su yi kokarin ganin an sako wadanda aka yi garkuwa da su da kuma gaggauta samar da hanyoyin dakile ci gaba da kai hare-hare.

Sanarwar ta jajantawa wadanda suka jikkata, iyalan wadanda aka kama tare da yi musu fatan samun sauki da kuma dawowar ‘yan uwansu lafiya.

A ranar Litinin din da ta gabata ne dai aka yi awon gaba da shugaban kotun al’adun gargajiya na yankin Igueben, Precious Aigbonoga da tsohon dan majalisar dokokin Edo, Festus Edughele a wani lamari daban-daban.

Jami’in shari’ar dai ita ce matar Afebu Aigbonoga, dan takarar majalisar wakilai na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a mazabar Etsako ta Yamma 1.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp