Kungiyar Malaman Makarantun Kimiyya da Fasaha (ASUP) da ke Kwalejin Kimiyya ta Tarayya na Ekowe a Jihar Bayelsa, ta umarci mambobinta da su shiga yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar Litinin, saboda rashin aiwatar da ƙarin matsayi da alawus-alawus na koyarwa da kuma rashin kyawun yanayin aiki.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Comrade Agada Franklin da babban sakataren kungiyar Justin Ikirigo suka bai wa manema labarai a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Kungiyar ta ce ta ɗauki matakin shiga yajin aikin ne a wani taron gaggawa da ta gudanar kan wasu batutuwa da ke da illa ga mambobin kungiyar.
Sanarwar ta sake bayyana cewa shiga yajin aikin ba makawa saboda kungiyar ta taɓa dakatar da yajin aikin gargaɗi a ranar 31 ga watan Agustan 2022, sannan ta fitar da tunatarwa a ranakun 6 ga Disamba, 2022 da 10 ga Maris, 2023.