fidelitybank

Kungiyar Malaman makarantun kimiyya da fasaha za tsunduma yajin aiki

Date:

Kungiyar Malaman Makarantun Kimiyya da Fasaha (ASUP) da ke Kwalejin Kimiyya ta Tarayya na Ekowe a Jihar Bayelsa, ta umarci mambobinta da su shiga yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar Litinin, saboda rashin aiwatar da ƙarin matsayi da alawus-alawus na koyarwa da kuma rashin kyawun yanayin aiki.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Comrade Agada Franklin da babban sakataren kungiyar Justin Ikirigo suka bai wa manema labarai a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kungiyar ta ce ta ɗauki matakin shiga yajin aikin ne a wani taron gaggawa da ta gudanar kan wasu batutuwa da ke da illa ga mambobin kungiyar.

Sanarwar ta sake bayyana cewa shiga yajin aikin ba makawa saboda kungiyar ta taɓa dakatar da yajin aikin gargaɗi a ranar 31 ga watan Agustan 2022, sannan ta fitar da tunatarwa a ranakun 6 ga Disamba, 2022 da 10 ga Maris, 2023.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp