Kungiyar limaman majami’a ta Najeriya reshen Kudu-maso-Kudu ta nuna goyon bayan ta ga tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, a matsayin dan takarar ta na shugaban kasa a zaben 2023.
Malaman sun bayyana cewa Najeriya na bukatar dan siyasa a matsayin Tinubu domin ya zama shugaban Najeriya.
Malaman sun bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da babban kodinetan na jihar, Joseph Francis na Delta, da mataimakin kodineta, Apostle Chris Ebhodaghe na Edo, suka bayar ga manema labarai a Benin ranar Litinin.
Kungiyar ta bukaci mambobin jam’iyyar APC da su tabbatar da cewa Tinubu ya samu tikitin jam’iyyar.
Sun yi nuni da cewa, Tinubu zai kawo wa harkokin siyasa ci gaba, domin bai shiga cikin gwamnati ba a shekaru 15 da suka wuce, sai dai kawai shugaban jam’iyyar na kasa.
Sanarwar ta ce, Najeriya ta rabu bisa kabilanci da addini, kuma tana bukatar dan Najeriya da aka yi wa kabilanci wanda zai iya karbar kowa.