Kungiyar Kwadago NLC, za ta gudanar da wani taron gaggawa na majalisar zartarwa ta kasa game da shirin da take yi na shiga yajin aikin sai baba ta gani.
Wannan matakin ya biyo bayan cikar wa’adin kwanaki 21 da ƙungiyar ta bai wa gwamnati don biya musu buƙatu.
A cikin wata takardar gayyata da ta tura wa manema labaru a yau Talata, NLC ta ce za ta gana da manema labarun a ranar ta yau domin tabbatar masu da matsayar da ta cimma.
Ƙungiyar dai a baya ta shirya yajin aikin gama-gari da ta gudanar a ranakun 5 da 6 ga watan Satumba, saboda tsadar rayuwar da ƙasar ta shiga sakamakon cire tallafin man da shugaba Bola Tinubu ya yi.
Bugu da kari, kimanin wata guda da ya gabata, ƙungiyar ƙwadagon sun shiga yajin aikin don magance irin matsalolin da suka shafi tsadar rayuwa, sai dai daga bisani suka dakatar da yajin aikin bayan tattaunawa da shugaba Bola Tinubu.