Kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar Neja, ta dakatar da yajin aikin da ma’aikatan kananan hukumomi da na jihohi suka fara makonni biyu da suka gabata kan biyan albashin ma’aikata.
An dakatar da yajin aikin masana’antar daga tsakar daren Alhamis, Maris 24, 2022.
Kungiyar a cikin wata sanarwa da ta fitar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar na jihar, Kwamared Yakubu Garba, ta ce, dakatarwar ta biyo bayan wasu tarurrukan da gwamnatin jihar Neja ta gudanar da kungiyar kwadago, wanda ya haifar da sakamako mai kyau.
Garba ya ce, gwamnatin jihar ta amince ta fara biyan ‘yan fansho na Jiha, ta amince da yin amfani da wasu hanyoyi cikin kankanin lokaci, domin magance koma bayan kudaden gratuti na jihar da na kananan hukumomi, da kuma yadda za a yi amfani da su.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, gwamnati ta amince da wani bangare na cin hanci da rashawa da aka cire na wasu kamfanoni da kudi Naira milliyan 200, kuma ta amince da aika da kudi N100m a kowane wata domi,n tafka kura-kuran da aka samu na cirar kashi na uku da kuma biyan 100% na watan Fabrairu, 2022. albashin ma’aikata a fadin kananan hukumomi 25 a jihar Neja.
Sakamakon haka, kungiyar ta c,e gwamnatin jihar Neja, shugabannin kananan hukumomi 25 da kungiyar kwadago sun amince da ci gaba da tattaunawa, domin samar da mafita mai dorewa ga sauran bukatu na ma’aikatan kananan hukumomin tare da kammala karshen 31 ga Mayu, 2022.