fidelitybank

Kungiyar Kwadago ta caccaki Gwamnatin Tinubu a kan cire tallafin man fetur

Date:

Ƙungiyar Ƙwadago ta caccaki Asusun Lamuni, bisa maganar cewa ba ita ba ce ta shawarci gwamnatin Najeriya ta cire tallafin man fetur.

A wata sanarwa da NLC ta fitar a ranar Lahadi, wanda shugabanta Joe Ajaero ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta soki IMF bisa shawarwarin da take bayarwa a matsayin hanyoyin farfaɗio da tattalin arziki, waɗanda a cewarta su ne suka jawo wahala da tsayar komai cak a Najeriya da sauran ƙasashen da suke bin irin shawarwarin kamar yadda Channels ta ruwaito.

Tun da farko, a wani taron manema labarai na IMF da bankin duniya da aka yi a Washington DC, darakta yankin Afirka na IMF, Abebe Selassie, ya ce cire tallafin man fetur mataki ne da gwwamnatin Najeriya ta ɗauka a cikin gida.

“Wannan maganar ta IMF cewa a cikin gida ne aka ɗauki matakin cire tallafin mai, amma sai ba ta bayyana irin rawar da suka takawa wajen jula akalar dokokin ƙananan ƙasashe ba. Duk da ƙoƙarin da IMF ke yi nesanta kanta da cire tallafin, mu mun san ita ce kan gaba wajen kira da a cire tallafin man fetur domin inganta tattalin arzikin irin waɗannan ƙasashen.

“IMF na so ta nesanta kanta ne saboda matsalolin da suka biyo baya, amma ai ƴan Najeriya ba wawaye ba ne. Mun riga mun san yadda matakan da shawawarinsu suka jefa Najeriya da ma wasu Afirka cikin damuwa,” in ji ƙungiyar.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp