fidelitybank

Kungiyar Kwadago ta caccaki Gwamnatin Tinubu a kan cire tallafin man fetur

Date:

Ƙungiyar Ƙwadago ta caccaki Asusun Lamuni, bisa maganar cewa ba ita ba ce ta shawarci gwamnatin Najeriya ta cire tallafin man fetur.

A wata sanarwa da NLC ta fitar a ranar Lahadi, wanda shugabanta Joe Ajaero ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta soki IMF bisa shawarwarin da take bayarwa a matsayin hanyoyin farfaɗio da tattalin arziki, waɗanda a cewarta su ne suka jawo wahala da tsayar komai cak a Najeriya da sauran ƙasashen da suke bin irin shawarwarin kamar yadda Channels ta ruwaito.

Tun da farko, a wani taron manema labarai na IMF da bankin duniya da aka yi a Washington DC, darakta yankin Afirka na IMF, Abebe Selassie, ya ce cire tallafin man fetur mataki ne da gwwamnatin Najeriya ta ɗauka a cikin gida.

“Wannan maganar ta IMF cewa a cikin gida ne aka ɗauki matakin cire tallafin mai, amma sai ba ta bayyana irin rawar da suka takawa wajen jula akalar dokokin ƙananan ƙasashe ba. Duk da ƙoƙarin da IMF ke yi nesanta kanta da cire tallafin, mu mun san ita ce kan gaba wajen kira da a cire tallafin man fetur domin inganta tattalin arzikin irin waɗannan ƙasashen.

“IMF na so ta nesanta kanta ne saboda matsalolin da suka biyo baya, amma ai ƴan Najeriya ba wawaye ba ne. Mun riga mun san yadda matakan da shawawarinsu suka jefa Najeriya da ma wasu Afirka cikin damuwa,” in ji ƙungiyar.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp