Kungiyar kiristoci ta Najeriya, CAN reshen Filato ta yi wani gangami domin nuna rashin jin daɗinta kan kashe-kashen da ke wakana a jihar da wasu sassan ƙasar.
Gangamin da aka yi wa taken ‘Tattakin zaman lafiya a Filato’ na gudana ne ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar CAN, Rabaran Polycarp Lubo bisa rakiyar shugaban cocin ECWA, Rabarand Dr Stephen Panya.
Gwamnan jihar ta Filato Caleb Mutfwang ya karɓi baƙuncin masu zanga-zangar a fadarsa da ke Rayfield.
Jihar Filato dai a baya-bayan nan na fuskantar hare-haren ta’addanci inda aka kashe sama da mutum 200 a jajiberin kirsimeti a hare-haren da aka kai a ƙananan hukumomin Bokkos da Barikin Ladi.
An ƙona gidaje da dama da gonaki a hare-haren da aka shafe dare ana kai wa, an kuma samu mutane da dama da suka jikkata.
Hare-haren da aka kai kan ƙananan hukumomin ya fusata al’ummar Najeriya da ma na ƙasashen duniya inda gwamnan ya caccaki sojoji kan jan ƙafar da suka yi wajen kai ɗauki.
Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya kai ziyara a yankunan bayan hare-haren inda gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin kawo ƙarshen zubar da jinin, sai dai mutane na neman gwamnati ta ɗauki matakan da suka kamata domin kare al’umma a maimakon ɗaukar mataki bayan afkuwar hare-hare.