fidelitybank

Kungiyar kiristoci ta yi zanga-zanga a kan kisan Filato

Date:

Kungiyar kiristoci ta Najeriya, CAN reshen Filato ta yi wani gangami domin nuna rashin jin daɗinta kan kashe-kashen da ke wakana a jihar da wasu sassan ƙasar.

Gangamin da aka yi wa taken ‘Tattakin zaman lafiya a Filato’ na gudana ne ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar CAN, Rabaran Polycarp Lubo bisa rakiyar shugaban cocin ECWA, Rabarand Dr Stephen Panya.

Gwamnan jihar ta Filato Caleb Mutfwang ya karɓi baƙuncin masu zanga-zangar a fadarsa da ke Rayfield.

Jihar Filato dai a baya-bayan nan na fuskantar hare-haren ta’addanci inda aka kashe sama da mutum 200 a jajiberin kirsimeti a hare-haren da aka kai a ƙananan hukumomin Bokkos da Barikin Ladi.

An ƙona gidaje da dama da gonaki a hare-haren da aka shafe dare ana kai wa, an kuma samu mutane da dama da suka jikkata.

Hare-haren da aka kai kan ƙananan hukumomin ya fusata al’ummar Najeriya da ma na ƙasashen duniya inda gwamnan ya caccaki sojoji kan jan ƙafar da suka yi wajen kai ɗauki.

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya kai ziyara a yankunan bayan hare-haren inda gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin kawo ƙarshen zubar da jinin, sai dai mutane na neman gwamnati ta ɗauki matakan da suka kamata domin kare al’umma a maimakon ɗaukar mataki bayan afkuwar hare-hare.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp