fidelitybank

Kungiyar Kiristoci ta CAN ta zabi sabon shugaba

Date:

An zabi Rabaran Daniel Chukwudumebi Okoh, a matsayin sabon shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya, CAN.

Sanarwar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren kungiyar ta CAN, Mista Joseph Daramola ya fitar.

Okoh shine Babban Sufeto na Cocin Christ Holy Church, wanda kuma ake kira Nation Builders (Odozi-Obodo).

A halin da ake ciki, PRNigeria ta tattaro cewa, haifaffen Kano kuma dan asalin jihar Ribas, Most Rev. Daniel Okoh, dan Najeriya ne da ya kawar da kabilanci wanda ya kulla abota tsakanin addini da kabilanci, ba a Najeriya kadai ba har ma a fadin duniya. Yana shiryawa da shiga cikin tattaunawa da shirye-shiryen da za su samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin duniya da ci gaba mai dorewa.

Rabaran Okon na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun sabani na addini da tashin hankali musamman tsakanin Kirista da Musulmi.

Ana sa ran sabon shugaban kungiyar ta CAN, tare da gogewar da ya samu a tattaunawar tsakanin addinai, zai dauki matakan rage takun saka tsakanin mabiya addinan, musamman tsakanin Kirista da Musulmi a kasar.

An haifi Okoh a ranar 12 ga Nuwamba, 1963 a Kano, iyayen Kirista. Shi dan asalin garin Ndoni ne a karamar hukumar Ogba/Egbema/Ndoni da ke jihar Ribas a Najeriya.

Ya auri Ngozi kuma sun sami ‘ya’ya hudu. Archbishop Daniel Okoh samfur ne na sanannen makarantar Dennis Memorial Grammar School, Onitsha.

A 1988, ya sauke karatu daga Jami’ar Port-Harcourt a digiri na biyu a fannin Kimiyyar Siyasa da Ilimi.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp