fidelitybank

Kungiyar kare hakkin bil adama ta yi Allah wadai da hukuncin da aka yi wa ‘yan TikTok

Date:

Kungiyar kare hakkin bil-adama ta Amnesty International ta yi Allah wadai da hukuncin da aka yanke wa matasan nan biyu masu amfani da shafin TikTok a jihar Kano saboda bata sunan gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje.

Tun da farko dai matasan biyu masu suna Mubarak Muhammad alias wanda aka fi sani da Uniquepikin a shafin, da kuma Nazifi Muhammad, sun amsa laifinsu tare da neman sassauci daga kotu.

An kuma yanke musu hukuncin bulala 20 kowannensu da kuma biyan tarar 10,000 tare da share kotu na tsawon wata guda.

Kungiyar ta Amnesty International ta ce kama yaran tare da tsare su a gidan yari kafin a yanke musu hukunci abu ne da ya saba wa doka, ta kuma yi kira da a saki yaran ba tare da wani sharadi ba.

Haka kuma kungiyar ta zargi alkalin da cewa mai bin umarnin gwamnatin jihar ne.

Tuni dai aka fara zartar da wasu daga cikin hukunce-hukunce, inda aka yi musu bulalar a gaban jama’ar da ke harabar kotun, sannan kuma sun biya tarar.

Lauyan matasan ya ce sun amince da hukuncin kotun, dan haka ba za su daukaka kara ba.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp