fidelitybank

Kungiyar kare hakkin bil adama ta yi Allah wadai da hukuncin da aka yi wa ‘yan TikTok

Date:

Kungiyar kare hakkin bil-adama ta Amnesty International ta yi Allah wadai da hukuncin da aka yanke wa matasan nan biyu masu amfani da shafin TikTok a jihar Kano saboda bata sunan gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje.

Tun da farko dai matasan biyu masu suna Mubarak Muhammad alias wanda aka fi sani da Uniquepikin a shafin, da kuma Nazifi Muhammad, sun amsa laifinsu tare da neman sassauci daga kotu.

An kuma yanke musu hukuncin bulala 20 kowannensu da kuma biyan tarar 10,000 tare da share kotu na tsawon wata guda.

Kungiyar ta Amnesty International ta ce kama yaran tare da tsare su a gidan yari kafin a yanke musu hukunci abu ne da ya saba wa doka, ta kuma yi kira da a saki yaran ba tare da wani sharadi ba.

Haka kuma kungiyar ta zargi alkalin da cewa mai bin umarnin gwamnatin jihar ne.

Tuni dai aka fara zartar da wasu daga cikin hukunce-hukunce, inda aka yi musu bulalar a gaban jama’ar da ke harabar kotun, sannan kuma sun biya tarar.

Lauyan matasan ya ce sun amince da hukuncin kotun, dan haka ba za su daukaka kara ba.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp