Kungiyar Gwamnonin Progressive Governors Forum (PGF), ta bi sahun ‘yan Najeriya wajen taya Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje murnar cika shekaru 73 da haihuwa.
A cikin wata sanarwa da shugaban PGF, Abubakar Atiku Bagudu ya fitar, ya yabawa jagorancin Ganduje da jajircewarsa wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba.
Ya ce, “Gwamnan Progressive Governors Forum (PGF) na tare da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano domin bikin cikarsa shekaru 73 a duniya. Tare da al’ummar jihar Kano, da sauran ‘yan Najeriya masu kishin kasa, muna taya ku da iyalanku murnar wannan rana ta musamman.
“Muna yaba wa jagoranci, hangen nesa da kuma jajircewar ku wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba a dunkule, karkashin jagorancin jam’iyyar mu ta APC. Muna godiya da irin gudunmawar da kuke baiwa tawagar Gwamnonin Cigabanmu ta hanyar basirar ku da kuma jajircewar ku akan hanyoyin tafiyar da harkokin mulki a jihar Kano da ma a matakin kasa baki daya. A matsayinka na Gwamnan Jihar Kano, ta hanyar duk wasu tsare-tsare na ci gaba da gwamnatinka karkashin jam’iyyar APC ke aiwatarwa, muna tabbatar da cewa kai shugaba ne na gaskiya mai son ci gaba da kirkire-kirkire.
“A yayin da muke murna da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, muna kuma kara jaddada aniyarmu ta hadin gwiwa wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa karfin jihohinmu masu ci gaba wajen samar da ayyukan yi, rage rashin daidaito da kuma rage radadin talauci a Najeriya.
“Sai kuma ina taya Mai Girma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje murnar zagayowar ranar haihuwarsa.”