fidelitybank

Kungiyar Gwamnoni sun taya Ganduje murnar cika shekaru 73

Date:

Kungiyar Gwamnonin Progressive Governors Forum (PGF), ta bi sahun ‘yan Najeriya wajen taya Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje murnar cika shekaru 73 da haihuwa.

A cikin wata sanarwa da shugaban PGF, Abubakar Atiku Bagudu ya fitar, ya yabawa jagorancin Ganduje da jajircewarsa wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba.

Ya ce, “Gwamnan Progressive Governors Forum (PGF) na tare da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano domin bikin cikarsa shekaru 73 a duniya. Tare da al’ummar jihar Kano, da sauran ‘yan Najeriya masu kishin kasa, muna taya ku da iyalanku murnar wannan rana ta musamman.

“Muna yaba wa jagoranci, hangen nesa da kuma jajircewar ku wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba a dunkule, karkashin jagorancin jam’iyyar mu ta APC. Muna godiya da irin gudunmawar da kuke baiwa tawagar Gwamnonin Cigabanmu ta hanyar basirar ku da kuma jajircewar ku akan hanyoyin tafiyar da harkokin mulki a jihar Kano da ma a matakin kasa baki daya. A matsayinka na Gwamnan Jihar Kano, ta hanyar duk wasu tsare-tsare na ci gaba da gwamnatinka karkashin jam’iyyar APC ke aiwatarwa, muna tabbatar da cewa kai shugaba ne na gaskiya mai son ci gaba da kirkire-kirkire.

“A yayin da muke murna da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, muna kuma kara jaddada aniyarmu ta hadin gwiwa wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa karfin jihohinmu masu ci gaba wajen samar da ayyukan yi, rage rashin daidaito da kuma rage radadin talauci a Najeriya.

“Sai kuma ina taya Mai Girma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje murnar zagayowar ranar haihuwarsa.”

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...
X whatsapp