fidelitybank

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Date:

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu kan rasuwar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga watan Yulin shekarar 2025 a birnin Landan.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, wanda shugabanta, Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya fitar, ya ce Buhari tamkar uba yake a gare su.

“Muna miƙa ta’aziyarmu ga Shugaban Najeriya Bola Tinubu da iyalai da ƴanuwa da mutanen jihar Katsina da ma ƴan Najeriya baki ɗaya bisa wannan babban rashin da aka yi.”

Gwamnonin sun ce Buhari abin alfaharin yankinsu ne, “wanda ya ƙarar da rasyuwarsa wajen hidima da sadaukar da kansa wajen ciyar da Najeriya gaba.”

“Saboda wannan ne ƙungiyar gwmnonin arewa maso yamma suka amince da ayyana ranar Talata, 5 ga watan Yulin 2025 a matsayin ranar hutu domin jimamin rasuwar mamacin,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Dikko Radda ya ce gawar Buhari za ta isa Katsina a gobe Talata da misalin ƙarfe 12, sannan a gudanar da jana’izar da misalin ƙarfe biyu na rana.

“Muna kira ga dukkan ƴan Najeriya su yi masa addu’a. Allah ya jiƙansa, sannan muna addu’ar Allah ya ba iyalana da ma dukkan ƴan ƙasar juriyar rashinsa.”

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp