fidelitybank

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Date:

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu kan rasuwar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga watan Yulin shekarar 2025 a birnin Landan.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, wanda shugabanta, Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya fitar, ya ce Buhari tamkar uba yake a gare su.

“Muna miƙa ta’aziyarmu ga Shugaban Najeriya Bola Tinubu da iyalai da ƴanuwa da mutanen jihar Katsina da ma ƴan Najeriya baki ɗaya bisa wannan babban rashin da aka yi.”

Gwamnonin sun ce Buhari abin alfaharin yankinsu ne, “wanda ya ƙarar da rasyuwarsa wajen hidima da sadaukar da kansa wajen ciyar da Najeriya gaba.”

“Saboda wannan ne ƙungiyar gwmnonin arewa maso yamma suka amince da ayyana ranar Talata, 5 ga watan Yulin 2025 a matsayin ranar hutu domin jimamin rasuwar mamacin,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Dikko Radda ya ce gawar Buhari za ta isa Katsina a gobe Talata da misalin ƙarfe 12, sannan a gudanar da jana’izar da misalin ƙarfe biyu na rana.

“Muna kira ga dukkan ƴan Najeriya su yi masa addu’a. Allah ya jiƙansa, sannan muna addu’ar Allah ya ba iyalana da ma dukkan ƴan ƙasar juriyar rashinsa.”

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...

Na yafe wa Buhari duk abun da ya yi min – Buba Galadima

Buba Galadima, wanda tsohon abokin marigayi Muhammadu Buhari ne...

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...
X whatsapp