fidelitybank

Kungiyar gwamnoni da Buhari sun gana da Emefiele

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi ganawar sirri da shugaban ƙungiyar gwamnoni ta kasa, Aminu Waziri Tambuwal, da shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC Atiku Bagudu kan matsalar ƙarancin sabbin takardun kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

Daga cikin waɗanda suka halarci zaman har da gwamnan Babban Bankin ƙasar Godwin Emefiele da shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasar Abdulrasheed Bawa da kuma babban hafsan hafsoshin tsaron ƙasar Janar Lucky Irabor.

An yi ganawar ne a fadar shugaban ƙasar da ke Abuja.

Karanta Wannan: An jibge jami’an tsaro a ofishin CBN

Da farko an tsara zaman da ƙungiyar gwamnonin ƙasar, to sai dai daga baya an soke zama da duka gwamnonin sakamakon wasu dalilai da ba a bayyana ba.

Bayyanar gwamnan Babban Bankin a ganawar alama ce da ke nuna cewa an tsara zaman ne domin tattauna batun matsalar ƙarancin kuɗi, da ke fuskantar suka daga ‘yan ƙasar, ciki har da gwamnonin ƙasar.

A makon da ya gabata ne dai shugaban ƙasar ya gana da ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, inda wasu daga cikin gwamnonin suka yi kira ga shugaban ƙasar da ya shiga tsakani domin bayar da dama a ci gaba da amfani da tsoffi da abbin takardun kuɗin a faɗin kasar.

To sai dai rahotonni sun ce shugaban ƙasar ya yi watsi da buƙatar kasancewar kotu ta haramta wa gamnati sake ƙara wa’adin daga ranar 10 ga watan Fabrairu.

Wasu majiyoyin a fadar shugaban ƙasar sun tabbatar da cewa shugaban ƙasar na kaffa-kaffa, kada ayi masa kallon mai watsi da dokoki.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp