fidelitybank

Kungiyar gwamnoni da Buhari sun gana da Emefiele

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi ganawar sirri da shugaban ƙungiyar gwamnoni ta kasa, Aminu Waziri Tambuwal, da shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC Atiku Bagudu kan matsalar ƙarancin sabbin takardun kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

Daga cikin waɗanda suka halarci zaman har da gwamnan Babban Bankin ƙasar Godwin Emefiele da shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ƙasar Abdulrasheed Bawa da kuma babban hafsan hafsoshin tsaron ƙasar Janar Lucky Irabor.

An yi ganawar ne a fadar shugaban ƙasar da ke Abuja.

Karanta Wannan: An jibge jami’an tsaro a ofishin CBN

Da farko an tsara zaman da ƙungiyar gwamnonin ƙasar, to sai dai daga baya an soke zama da duka gwamnonin sakamakon wasu dalilai da ba a bayyana ba.

Bayyanar gwamnan Babban Bankin a ganawar alama ce da ke nuna cewa an tsara zaman ne domin tattauna batun matsalar ƙarancin kuɗi, da ke fuskantar suka daga ‘yan ƙasar, ciki har da gwamnonin ƙasar.

A makon da ya gabata ne dai shugaban ƙasar ya gana da ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, inda wasu daga cikin gwamnonin suka yi kira ga shugaban ƙasar da ya shiga tsakani domin bayar da dama a ci gaba da amfani da tsoffi da abbin takardun kuɗin a faɗin kasar.

To sai dai rahotonni sun ce shugaban ƙasar ya yi watsi da buƙatar kasancewar kotu ta haramta wa gamnati sake ƙara wa’adin daga ranar 10 ga watan Fabrairu.

Wasu majiyoyin a fadar shugaban ƙasar sun tabbatar da cewa shugaban ƙasar na kaffa-kaffa, kada ayi masa kallon mai watsi da dokoki.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp