Alhassan Yahaya, mataimakin shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), ya zama sabon shugaban kungiyar na kasa.
Ya lashe zaben ne da kuri’u 436, inda ya doke Dele Atunbi, Ma’ajin Kasa mai barin gado, wanda ya samu kuri’u 97, da Garba Muhammad, wanda ya samu kuri’u 39.
Wakilai 602 daga shiyyoyin Najeriya shida da suka hada da babban birnin tarayya, sun hallara a Owerri, babban birnin jihar Imo, domin zaben sabon shugaban kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ).
Wannan sabon shugabancin zai tafiyar da harkokin kungiyar na tsawon shekaru uku masu zuwa.
Nasarar Yahaya ta zama sabon babi ga NUJ, kuma ana sa ran zai jagoranci kungiyar wajen inganta jin dadin ‘yan jarida da kuma kiyaye ka’idojin aikin jarida na gari.
Tun da farko Comrade Christopher Isiguzo, shugaban NUJ mai barin gado na kasa, ya bada tabbacin mika mulki cikin kwanciyar hankali, inda ya bayyana cewa ba zai tsoma baki a harkokin tafiyar da sabbin shugabannin ba.