fidelitybank

Kujerar shugaban marasa rinjaye ta haifar da cacar baka a majalisa

Date:

An samu takaddama a majalisar dattijai, bayan sanar da nadin shugabanni a bangaren marasa rinjaye da Shugaba Majalisar Godswill Akpabio ya yi.

Kujerar shugaban marasa rinjaye da ta mai tsawatarwa a bangaren marasa rinjaye sun kasance babu kowa tun bayan da kotun daukaka kara ta soke zaben Sanata Simon Davou Mwadkwon na PDP da Darlington Nwokocha na LP.

Kotu ta soke zaben sanata Simon Mwadkwon inda ta ba da umarnin sake gudanar da zabe.

Tun a makon jiya ne sanatocin jam’iyyar PDP suka gudanar da wani taron gaggawa kan batun maye guraben shugabannin marasa rinjaye.

Jaridar Punch ta ambato Sanata Garba Maidoki wanda ya yi jawabi ga manema labarai bayan taron, na cewa ‘yan majalisa bangaren adawa sun amince da fitar da sabon shugaban marasa rinjaye daga arewa ta tsakiya.

Don haka, yayin zaman majalisar na Talata, Godswill Akpabio ya sanar da Abba Moro na PDP a matsayin shugaban marasa rinjaye, yayin da Osita Ngwu shi ma daga PDP zai kasance mai tsawatarwa a bangaren marasa rinjaye.

Shugaban majalisar ya ce sabbin shugabannin marasa rinjayen sun samu rinjayen goyon bayan takwarorinsu.

Da yake gabatar da wanai kudurin jan hankali, Sanata Okechukwu Ezea na jam’iyyar LP ya nuna rashin amincewa da rashin shigar da jam’iyyarsa a shugabancin marasa rinjaye, inda ya bayyana lamarin a matsayin rashin adalci ga jam’iyyun marasa rinjaye.

Ana cikin hargitsi ne, sai Sanata Tony Nwoyi na LP ya zargi Godswill Akpabio da nada wa jam’iyyun adawa shugabanci.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka Æ´an Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar HaÉ—in kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp