Sakataren gwamnatin tarrayar Najeriya, Sanata George Akume ya bukaci ƴan siysasa daga arewacin ƙasar da ke neman tsayawa takara a zaɓen shugaben 2027 su jira har sai 2031.
A cewarsa, lokacin shugaba Bola Tinubu ya kammala wa’adi na biyu na shugabancin Najeriya
Akume a hirarsa da gidan talabijin na TVC, ya ce daga kudancin Najeriya ne ya kamata a fitar da shugaban ƙasa a 2027.
“Shugaba Tinubu ɗan kudanci ne, kuma a bar shi ya kammala wa’adinsa na biyu. Duk wanda ke neman mulkin ƙasar daga arewa a 2027 ya jira zuwa 2031,” in ji Akume.
Ya ƙara da cewa ya kamata a bar ƴan kudu su yi mulki na shekara takwas daga nan sai a koma arewa. ‘Idan ba haka ba za a lalata ƙasar nan.’
Tun bayan da gwamnatin Tinubu ta soma yunƙurin yi wa dokar harajin ƙasar garan-bawul, gwamnatinsa ke fuskantar adawa daga arewacin ƙasar.