fidelitybank

Kugiyar Amnesty ya bukaci a saki masu zanga-zangar Endsars

Date:

Ƙungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International, ya bukaci a saki sauran mutane da ake rike da su cikin akuba sakamakon zanga-zangar Endsars.

Kirayen Amnesty na zuwa ne bayan sakin mutum 9 daga cikin gwamman masu zanga-zangar da ake garkame da su a fursunoni daban-daban na Najeriya.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, Amnesty ta ce binciken ta na watan Oktoban 2022 ya nuna cewa ana rike da sama da masu zanga-zanga 40.

Sanarwar ta kuma kara da cewa abin takaici shi ne ganin har yanzu anki yarda ‘yan uwa da lauyoyin masu zanga-zangar su gana.

Zanga-zangar ta EndSARS wadda aka fara a Legas da Abuja a watan Oktoban 2020, ta kuma fantsama zuwa wasu jihohin kasar, kafin daga bisani ta rikiÉ—e ta koma rikici, abun da ya janyo asarar rayuka da dukiyoyin jama’a.

Masu zanga-zangar sun zargi jami’an tsaro da buÉ—e masu wuta a Lekki da ke jihar Legas, wato cibiyar inda ake gudanar da zanga-zanar, abin da ya janyo jikkatar mutane da dama.

Zanga-zangar ta ja hankalin duniya sosai inda har shahararrun mutane a fadin duniya suka dinga tsoma baki suna nuna goyon baya ga masu yin ta.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp