Fadar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta ce, jahilci ne ya sa wasu ke ganin Shugaban Ƙasa ke jan-ƙafa wajen saka wa sabon ƙudirin dokar zaɓe hannu, wanda Majalisar Tarayya ta miƙa masa tun a watan Janairu.
A kwanan nan ne wasu ƙungiyoyin farar hula suka dinga sukar shugaban saboda bai saka wa sabon ƙudirin dokar hannu ba a karo na biyu bayan Majalisar Tarayyar ta yi mata kwaskwarima tare da sake aika wa Buhari.
Wata sanarwa da fadar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce, shugaban ƙasa na da kwana 30 domin yin nazari kan ƙudirin, kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya ba shi dama.
“Sai dai a tausaya musu saboda jahiltar Kundin Tsarin Mulki da suka yi saboda shugaban ƙasa na da kwana 30 da zai iya saka mata hannu ko kuma akasin hakan bayan Majalisa ta miƙa masa dokar,” in ji sanarwar.
“A bayyane take cewa an miƙa wa shugaban ƙasa ƙudirin ranar 31 ga watan Janairun 2022, abin da ke nufin gwamnati za ta iya nazari cikin tsanaki har zuwa 1 ga watan Maris kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya tanada.”
Tun farko Buhari ya ƙi amincewa da sabuwar dokar yana mai cewa ‘yan majalisar ba su ba wa jam’iyyu zaɓi ba wajen maganar zaɓen fitar da ‘yan takara, inda suka ce zaɓen ‘yar tinƙe kaɗai za a bi. Daga baya sun gyara sannan suka sake miƙa wa shugaban. In ji BBC.