fidelitybank

Kudirin dokar zabe: Rashin wayewa ne ya s wasu ke ganin Buhari na jan kafa

Date:

Fadar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta ce, jahilci ne ya sa wasu ke ganin Shugaban Ƙasa ke jan-ƙafa wajen saka wa sabon ƙudirin dokar zaɓe hannu, wanda Majalisar Tarayya ta miƙa masa tun a watan Janairu.

A kwanan nan ne wasu ƙungiyoyin farar hula suka dinga sukar shugaban saboda bai saka wa sabon ƙudirin dokar hannu ba a karo na biyu bayan Majalisar Tarayyar ta yi mata kwaskwarima tare da sake aika wa Buhari.

Wata sanarwa da fadar ta wallafa a shafinta na Twitter ta ce, shugaban ƙasa na da kwana 30 domin yin nazari kan ƙudirin, kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya ba shi dama.

“Sai dai a tausaya musu saboda jahiltar Kundin Tsarin Mulki da suka yi saboda shugaban ƙasa na da kwana 30 da zai iya saka mata hannu ko kuma akasin hakan bayan Majalisa ta miƙa masa dokar,” in ji sanarwar.

“A bayyane take cewa an miƙa wa shugaban ƙasa ƙudirin ranar 31 ga watan Janairun 2022, abin da ke nufin gwamnati za ta iya nazari cikin tsanaki har zuwa 1 ga watan Maris kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya tanada.”

Tun farko Buhari ya ƙi amincewa da sabuwar dokar yana mai cewa ‘yan majalisar ba su ba wa jam’iyyu zaɓi ba wajen maganar zaɓen fitar da ‘yan takara, inda suka ce zaɓen ‘yar tinƙe kaɗai za a bi. Daga baya sun gyara sannan suka sake miƙa wa shugaban. In ji BBC.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp