Yusuf Datti Baba-Ahmed, abokin takarar Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, ya ce, da a ce an yi amfani da rabin kudaden da aka kashe wajen baiwa wakilai na Delegate kudaden ga kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), da dukkanin al’amuranta sun daidaita.
Datti Baba-Ahmed, wanda aka bayyana a matsayin abokin takarar Obi a ranar Juma’a, ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook.
Ya ce, “Ya ku ‘yan uwa daliban Najeriya, kun kasance a gida na tsawon lokaci” Wannan batu na ASUU wani abu ne da ya dade shekaru da yawa, saboda har yanzu shugabanninmu ba su fahimci bukatar saka hannun jari a ci gaban bil’adama ba. Ilimi wani bangare ne na jarin dan adam, tsawon watanni yanzu saboda batun ASUU ku na gida.
“Yaya ‘ya’yanmu za su biya kudin makaranta na shekara hudu ko biyar, kuma bayan sun shafe tsawon shekaru a makaranta, za ka gano cewa, ba su taba yin karatu har tsawon shekaru 2 ba tare da tsangwama ba saboda batun ASUU. Amma duk da haka sun biya cikakken kwas na shekara hudu zuwa biyar!.
“Kudin da ake kashewa kan wakilai kadai na iya magance kashi 50% na yajin aikin Asuu”.
Datti Baba-Ahmed, tsohon dan majalisar dattawa ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ba da goyon baya ga yunkurinsu.