fidelitybank

Kudin da aka kashewa Daligate ya isa ya magance rikicin ASUU

Date:

Yusuf Datti Baba-Ahmed, abokin takarar Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, ya ce, da a ce an yi amfani da rabin kudaden da aka kashe wajen baiwa wakilai na Delegate kudaden ga kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), da dukkanin al’amuranta sun daidaita.

Datti Baba-Ahmed, wanda aka bayyana a matsayin abokin takarar Obi a ranar Juma’a, ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook.

Ya ce, “Ya ku ‘yan uwa daliban Najeriya, kun kasance a gida na tsawon lokaci” Wannan batu na ASUU wani abu ne da ya dade shekaru da yawa, saboda har yanzu shugabanninmu ba su fahimci bukatar saka hannun jari a ci gaban bil’adama ba. Ilimi wani bangare ne na jarin dan adam, tsawon watanni yanzu saboda batun ASUU ku na gida.

“Yaya ‘ya’yanmu za su biya kudin makaranta na shekara hudu ko biyar, kuma bayan sun shafe tsawon shekaru a makaranta, za ka gano cewa, ba su taba yin karatu har tsawon shekaru 2 ba tare da tsangwama ba saboda batun ASUU. Amma duk da haka sun biya cikakken kwas na shekara hudu zuwa biyar!.

“Kudin da ake kashewa kan wakilai kadai na iya magance kashi 50% na yajin aikin Asuu”.

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan majalisar dattawa ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ba da goyon baya ga yunkurinsu.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...
X whatsapp