Pa Ayo Adebanj,o ya roki ‘yan Najeriya da su zabi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, LP, Peter Obi, ranar Asabar.
Shugaban kungiyar Yarbawa koli, Afenifere ya zayyana kuri’u ga Obi a wata ganawa da kungiyar Atunluse Initiatives.
Dattijon ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar al’adu da siyasa ta Yarbawa a ranar Talata a Legas, kamar yadda NAN ta ruwaito.
Karanta Wannan: Zan magance rashin aikin yi ga matasa – Obi
Adebanjo ya ce jama’a na bukatar tsohon gwamnan Anambra don ceto Najeriya daga kangin talauci da rashin shugabanci.
“Duk ‘yan kasa suna da alhakin gwagwarmayar kwato ‘yancinsu ta hanyar zaben shugaban kasa na karshen mako,” in ji shi.
“Ba mu da kudi don yakar su, amma dole ne mu yi duk abin da ya dace don ‘yantar da kanmu,” in ji shi.
Adebanjo ya ci gaba da cewa, akwai yarjejeniyar da aka kulla cewa za a raba madafun iko a cibiyar tsakanin Arewa da Kudu.
Basaraken ya tuna cewa Kudu-maso-Yamma sun yi zamaninsu a karkashin Olusegun Obasanjo da kuma Arewa a karkashin Umaru Yar’Adua.
“Goodluck Jonathan ya yi nasa daga Kudu-maso-Kudu, ya koma Arewa. Yanzu idan muka dawo Kudu, a ba yankin Kudu-maso-Gabas da sunan adalci,” inji shi.
Shugaban kungiyar Atunluse, Akinsola Akinbobola da tawagarsa daga baya sun yi ganawar sirri da Adebanjo da sauran shugabannin kungiyar ta Afenifere.