fidelitybank

Ku zabi Peter Obi a ranar Asabar – Pa Ayo Adebanjo

Date:

Pa Ayo Adebanj,o ya roki ‘yan Najeriya da su zabi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, LP, Peter Obi, ranar Asabar.

Shugaban kungiyar Yarbawa koli, Afenifere ya zayyana kuri’u ga Obi a wata ganawa da kungiyar Atunluse Initiatives.

Dattijon ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar al’adu da siyasa ta Yarbawa a ranar Talata a Legas, kamar yadda NAN ta ruwaito.

Karanta Wannan: Zan magance rashin aikin yi ga matasa – Obi

Adebanjo ya ce jama’a na bukatar tsohon gwamnan Anambra don ceto Najeriya daga kangin talauci da rashin shugabanci.

“Duk ‘yan kasa suna da alhakin gwagwarmayar kwato ‘yancinsu ta hanyar zaben shugaban kasa na karshen mako,” in ji shi.

“Ba mu da kudi don yakar su, amma dole ne mu yi duk abin da ya dace don ‘yantar da kanmu,” in ji shi.

Adebanjo ya ci gaba da cewa, akwai yarjejeniyar da aka kulla cewa za a raba madafun iko a cibiyar tsakanin Arewa da Kudu.

Basaraken ya tuna cewa Kudu-maso-Yamma sun yi zamaninsu a karkashin Olusegun Obasanjo da kuma Arewa a karkashin Umaru Yar’Adua.

“Goodluck Jonathan ya yi nasa daga Kudu-maso-Kudu, ya koma Arewa. Yanzu idan muka dawo Kudu, a ba yankin Kudu-maso-Gabas da sunan adalci,” inji shi.

Shugaban kungiyar Atunluse, Akinsola Akinbobola da tawagarsa daga baya sun yi ganawar sirri da Adebanjo da sauran shugabannin kungiyar ta Afenifere.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp