Matar dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Mrs Titi Atiku Abubakar ta nemi mata ‘yan Najeria da su tuhume ta matukar mijinta ya gaza cika alkawuran kamfen da ya dauka idan ya gaji Buhari.
Ta bayyana cewa, Atiku ba zai watsar da yankin Kudu maso Yamma ba, domin ba Atiku kuri’u daidai yake da ba Yarbawa kuri’u, Daily Trust ta ruwaito.
Ta bayyana wannan ne a wani taron siyasa na mata da aka gudanar a jihar Ogun a birnin Abeokuta na jihar.
Matar Atiku ta ce, idan aka zabi mijinta, za ta zama Bayarbiya ta farko da ta zama uwar gidan shugaban kasa daga yankin Kudu maso Yamma.