fidelitybank

Ku taimake ni zan mutu a hannun DSS – Nnamdi Kanu

Date:

Jagoran ƙungiyar ƴan awaren Biyafara masu neman ɓallewa daga Najeriya, Nnamdi Kanu ya koka kan halin da yake ciki a hannun jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya bayyana gaban babbar kotu a ranar Talata domin ci gaba da sauraron ƙararsa kan tuhumar cin amanar ƙasa da ta’addanci.

Ana yi masa tuhume-tuhumen ne da suka shafi tayar da husuma da kuma cin amanar ƙasa sanadiyyar gwagwarmayar da ƙungiyarsa ke yi a gabashin Najeriya na ganin ta zama ƙasa mai cin gashin kanta.

A harabar kotun, Kanu ya ɗage rigarsa domin nuna cewa ba a bashi kulawar da ta kamata inda ya yi iƙirarin cewa “zan mutu a hannun DSS.”

Shugaban na Ipob ya nuna wani ɓangare na jikinsa da ke da tabo bayan da kotu ta ba shi damar magana game da buƙatarsa ta neman beli da kotun ta yi watsi da ita.

Kanu ya ce ya na fama da matsalar ciwon zuciya sai dai magugunan da ake ba shi a hannun DSS “ba su da amfani”.

Ya ƙara da cewa DSS ba ta ba shi damar ganin likitan da yake so ba.

“Zan mutu a hannun DSS kuma suna ba ni magani mara tasiri. Suna duba ni game da matsalar zuciya amma maganin da suke ba ni ba shi da amfani. Suna son na mutu a tsare,” in ji Nnamdi Kanu.

Jagoran na Ipob ya buƙaci kotun ta mayar da shi gidan gyaran hali na Kuje sai dai mai shari’a Nyako ta ce tana da ikon ajiye Kanu duk inda ta ga babu barazanar tsaro.

Mai shari’a Nyako ta nemi a ci gaba da tsare Kanu a hannun DSS.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp