fidelitybank

Ku shirya fuskantar matsin rayuwa – Gwmnatin Ghana

Date:

Mataimakin shugaban Ghana, Mahamudu Bawumia, ya gargadi ‘yan kasar a kan matsanancin halin tsadar rayuwa da za a shiga yayin da kasar ke neman bashin Asusun bayar da tallafi na duniya bayan da hauhawar farashi ta kai kashi 29.8 cikin dari a watan Yuni.

A ranar Laraba ne jami’an Asusun na IMF suka kammala ziyararsu domin nazarin irin yanayi da halin da tattalin arzikin kasar ke ciki tare kuma da tattaunawa kan tallafin.

Gwamnatin kasar ta dora alhakin halin da ake ciki a kan matsaloli na waje, wadanda suka hada da yakin Ukraine. In ji BBC.

Mista Bawumia ya gaya wa ‘yan jarida cewa : “Yayin da muke fatan a gaggauta kawo karshen yakin [Ukraine], dole ne mu san cewa abubuwa za su iya yin tsanani kafin a samu sauki. Wajibi ne mu shirya domin fuskantar hakan.”

Ya kara da cewa, ”Babban matakin gaggawa da ya kamata a dauka shi ne dawo da tsimi da tsantseni a kan kudi da basuka, wannan kuma zai kasance ne ta hanyar haraji da kudaden da gwamnati ke kashewa da kuma yin sauye-sauye.”

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla ÆŠanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An É—age jana’izar Aminu ÆŠantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da É—age jana'izar fitaccen É—ankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp