fidelitybank

Ku sauke ni idan na kasa tabuka abun arziki – Peter Obi

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, LP, Peter Obi, ya bayyana dalilin da ya kamata ‘yan Najeriya su sauke shi idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben shugaban kasa mai zuwa.

Obi ya ce ‘yan Najeriya su kore shi da abokin takararsa, Yusuf Datti Baba-Ahmed, idan suka karkatar da kasar nan ta hanyar da ba ta dace ba.

Da yake jawabi a wurin taron masu kira na kungiyar Support Group a Abuja, Obi ya yi gargadi kan kada kuri’ar zaben ‘yan siyasar da suka talauta ‘yan Najeriya miliyan 95.

Karanta Wannan: Mambobin mu ku dakatar da aikin ku – Kungiyar dillalan man fetur

Don haka, Obi ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi watsi da tsohon tsarin siyasar da ya kawo talauci da bashi.

Ya bukaci ‘yan Najeriya da su mallaki kasar daga tsohuwar tsarin siyasa.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya jajircewar sa kan aikin New Nigeria, yana mai jaddada cewa “Wannan aikin ku ne.”

Obi ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su bukaci masu rike da mukaman gwamnati da su dauki mataki domin dakile matsalar cin hanci da rashawa.

Da yake jaddada cewa “Za mu iya sa Najeriya ta yi aiki,” Obi ya ce: “Ni da abokina, Dokta Yusuf Datti Baba-Ahmed, a matsayin direbobin da aikinsu zai kai Nijeriya zuwa wata manufa ta zaman lafiya, hadin kai da ci gaba idan aka zabe ni a matsayin shugaban kasa. da mataimakin shugaban kasa a zabe mai zuwa na Fabrairu 25, ‘kore’ ni da mataimakina, Yusuf Datti Baba-Ahmed a duk lokacin da aka gano muna daukar ‘yan Najeriya wata hanya dabam.”

Ya yi tir da yadda ake fama da talauci a kasar, inda ya nanata cewa Najeriya ba ta da wani dalili da za a sanya ta a cikin kasashe matalauta na duniya.

“Duk abin da kasarmu ta samar a cikin shekaru goma da suka wuce shi ne talauci. A shekarar 2012, adadin ‘yan Najeriya da ke fama da talauci ya kai kusan miliyan 65. A yau, kusan miliyan 95 ne. Kuma wadanda suka haddasa shi suna neman a kara musu shekaru. Me za ayi?” Ya tambaya.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp