fidelitybank

Ku kori jami’an da baku da ƙwarin gwiwa a kan su – Rundunar Sojoji

Date:

Shelkwatar tsaro ta fitar da wani gargadi ga wasu jami’anta da ake zargi da nuna rashin da’a da nuna wasu munanan dabi’u.

Har ila yau, ta umurci shugabannin sojojin Najeriya, na ruwa da na sama, da su ‘kori’ jami’an da basu da kwarin guiwa a kansu, wajen sauke nauyin da ke kansu na hidimtawa kasa.

Umarnin na kunshe ne cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan 26 ga watan Mayun da ya gabata, mai dauke da sa hannun daraktan harkokin gudanarwa na ma’aikatar tsaron Najiyar Rear Admiral Muhammed Nagenu, a madadin babban hafsan hafsoshin tsaron kasar Janar Lucky Irabor.

Shima kakakin ma’aikatar Major Akpon ya tabbatar da wannan wasika, sai dai ya ce ba wai za a kori sojojin ban aa aiki, illa dai gargadi irin na gyara kayanka, domin a cewarsa dabiu irin wadannan na iya haifar a rashin kwarin guiwa a kansu, musamman ta fuskar tura su fagen fama don tunkarar matsalolin tsaron da suka addabi kasar.

Ta ce a yayin da take ke iya bakin kokarinta wajn yaki da matsalolin taron da ake fuskanta, rashin maida hankalin wadannan dakaru na iya maida hannun agog baya, a don haka ko su gyara, ko kuma yi musu ritayar, tunda zai rage babu wani zabi da ya wuce hakan.

Birgedya Janar Sani Usman Kuka Sheka, mai sharhi ne kan lamuran tsaro a Najriya, ya kuma ce akwai abubuwan cikin gida da wasu bata gari suke fita suna yadawa ga mutanen waje, ana haka a aikin damara, amma ba a korar mutum haka kurum, sai an bi wasu hanyoyi masu yawa, kuma in da hakkokin mutum sai an biya shi hakkokinsa.

Wannan dai na faruwa ne yayin da ake unkarar zabukan 2023, kuma a cewar Birgediya Janar Sani Usman Kuka Sheka, dama akan yi gargadi irin wannan a lokaci irin wannan da aka shiga harkokin siyas.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp