fidelitybank

Ku dauki makamai ku kare kan ku daga ‘yan bindiga – Gwamnan Bauchi

Date:

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya umarci al’umomin yankunan da aka kai wa hari a baya-bayan nan a yankin ƙaramar hukumar Alkaleri da su tashi tsaye, su nemi makamai domin su kare kansu daga farmakin ‘yan bindiga.

Jaridar Daily Trust, ta ambato gwamnan na faɗin haka a fadar hakimin Yelwan Duguri a lokacin da ya ziyarci ƙauyukan Rimi da Gwana da Yalwan Duguri domin jajanta musu game da hare-haren ‘yan bindiga.

Dagacin garin Yelwan Duguri, Alhaji Adamu Mohammed Duguri ya ce mutum 20 ne suka mutu a ƙauyen Rimi lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari garin.

Gwaman ya ce lamarin abu ne da ‘ba za a lamunta ba’ dan haka dole ayi duk abin da ya kamata, domin hana faruwar hakan a nan gaba.

”An san ku da jarunta, bai kamata ku bar mutanen nan su ci gaba da cutar da ku ba, dan haka ku kare garinku domin ƙwatar kawunanku, ya kamata ku tashi tseye, ku nemi makamai domin kare kanku”, in ji gwamnan.

Haka kuma ya shawarci mutanen da su zaƙulo ɓata-gari a cikin mutanen da ke haɗa kai da ‘yan bindiga, musamman waɗanda suke bai wa ‘yan bindigar bayanan sirri kan mutanen gari, yana mai cewa dole sai da ɗan gari akan ci gari.

Wannan dai ba shi ne karo na farko da wani gwamna a Najeriya ke umartar al’umma da su nemi makamai domin kare kansu ba.

Domin kuwa a shekarar 2021 ma gwamnan jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar Aminu Bello Masari ya umarci al’ummar jiharsa da su nemi makamai domin kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga.

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp