fidelitybank

Ku daina yin tattaki ba na so – Abba Kabir Yusuf

Date:

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Injiniya, Abba Kabir Yusuf, ya buƙaci masu yin doguwar tafiyar ƙafa domin nuna murnarsu kan samun nasarar zaɓe da ya yi, da cewa su daina.

A maimakon haka ya buƙace su da su yi masa addu’ar samun nasara a mulkinsa domin maido da ƙwarin gwiwar da ‘yan jihar suka rasa cikin shekaru takwas da suka gabata.

A wata sanarwa da zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar, mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawunsa Sanusi Bature Dawakin Tofa, Abba ya buƙaci magoya bayansa da ‘yan jam’iyyarsa ta NNPP da su yi masa addu’ar samun nasara a mulkinsa.

Sabon gwamnan ya ce yin addu’a kaɗai ta wadatar wajen nuna murna ga nasarar da ya yi a zaɓen na ranar Asabar, ba sai mutum ya shafe tafiyar kilomitoci masu yawa a ƙafa ba.

Musamman a cewar sanarawar, idan aka yi la’akari da halin rashin tsaro na matsalar ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, waɗanda ke barazana ga zirga-zirgar jama’a da kayayyaki a faɗin ƙasar.

Yayin da yake gode wa magoya bayansa na ciki da wajen jihar Kano, zaɓaɓɓen gwamnan ya buƙaci masu doguwar tafiyar ƙafa da su daina, domin kuwa a cewarsa hakan ba zai taimaka wajen magance tarin matsalolin da ke jiran sabuwar gwamnatinsa ba, kamar yadda ya bayyana.

A Najeriya dai matasa da dama kan jefa rayuwarsu cikin hatsari wajen yin doguwar tafiyar ƙafa domin taya wani gwaninsu murnar nasarar da ya yi ta lashe zaɓe.

Matsan da a lokuta da dama kan ƙare doguwar tafiyar ba tare da samun ganawa da gwanin nasu ko makusantansa ba.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp