Wani rahoto da hukumar tattara alƙaluman ta NBS ta fitar ranar Litinin, ya nuna irin girman matsalar tsaro a Najeriya musamman abin da ya shafi garkuwa da mutane.
Rahoton mai taken Laifukan da aka fuskanta da kuma jin ra’ayin mutanen kan sha’anin tsaro na 2024, ya ce tsakanin watan Mayun 2023 da Afrilun 2024, an kashe ƴan Najeriya 614,937 sannan an yi garkuwa da mutum miliyan 2,235,954.
Rahoton ya kuma bayyana cewa an biya masu garkuwa da mutane kuɗin fansar da suka kai yawan naira tiriliyan 2.2, kuma hakan na nufin akan biyu naira miliyan 2.7 ga kowane mutum.