fidelitybank

Kowa zai koma gona saboda zan fatattaki ‘yan fashin daji – Tinubu

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu, ya ce, zai kawo karshen sace-sacen mutane, fashi da makami da sauran miyagun ayyuka idan aka zabe shi a zaben 2023 mai zuwa.

Tinubu ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake jawabi ga dimbin jama’a a wajen gangamin jam’iyyar APC a Dutse, babban birnin jihar Jigawa, ranar Asabar.

Ya ce Najeriya za ta shawo kan dukkan matsalolinta idan aka zabe ta a matsayin shugaban kasa.

“Insha Allahu Najeriya za ta samu ci gaba, za mu kawo karshen tashe-tashen hankula, za mu kawo karshen sace-sacen jama’a da sauran miyagun ayyuka.

“Za ku iya zuwa gonakinku duk tsawon lokaci ba tare da tsoron sace-sace, yin fashi da kuma biyan kudin fansa ba.

“Ku zabe ni ku zabe ni don ci gaba, hadin kai, da wadata,” in ji Tinubu.

Shima da yake jawabi, Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya ce taron ya isa shaida cewa mutanen jihar sun yi amanna da gwamnatin APC.

“Wannan ya nuna karara cewa Jigawa ta APC ce domin har wasu daga cikin ‘yan takarar jam’iyyun adawa sun fara watsi da takararsu sun shiga kungiyar da ta yi nasara.

“Uba da dansa ne suka rage a jam’iyyar PDP ta Jigawa,” Gwamna Badaru ya bayyana.

Don haka ya bukaci al’ummar jihar da su fito kwansu da kwarkwata domin kada kuri’a ga daukacin ‘yan takarar jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp