fidelitybank

Kowa ya zabi ra’ayin sa – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammdu Buhari, ya shawarci ‘yan ƙasa da su bi ra’ayinsu wajen zaɓar shugabanni na gari, a ɓangaren zartarwa da na majalisa, yana mai cewa zamanin sayen ƙuri’a ya wuce.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Malam Garba Shehu ya fitar, jim kaɗan bayan shugaban ƙsar ya kaɗa ƙuri’a, Muhammadu Buhari ya ce a yanzu mutane sun waye da zaɓen ra’ayinsu.

“Ina sane yanzu ba kamar da ba ne, mutane ba su da kuɗin da za su ja ra’ayin masu kaɗa ƙuria, kamar yadda suke yi a baya. A yanzu idan mutum ya kawo kuɗi, mutane za su karɓa kuma su zaɓi ra’ayinsu.

Karanta Wannan: Buhari ya kada kuri’arsa a Daura

Shugaba Buhari ya yaba wa kafofin yaɗa labaran ƙasar bisa rawar da ya ce sun taka wajen wayar da kan ‘yan ƙasar wajen sanin haƙƙokinsu a matsayinsu na ‘yan ƙasa, tare da samar musu kafar kalubalantar shugabanninsu kan alƙawuran da suka ɗaukar musu.

”Kafofin yaɗa labarai suna yin abin da ya dace wajen wayar da kan mutane, tare da ba su damar tofa albarkacin bakinsu. Za ka ji ana yi wa shugabanni tambayoyi masu tsauri a lokutan da ake hira da su a gidajen talabijin da radiyo da sauran kafofi, kuma a kodayaushe ‘yan jarida na tabbatar da cewa an amsa waɗannan tambayoyi”.

Daga ƙarshe shugaban ya ce bai yi mamakin nasarar da Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaɓen shugaban ƙasar da ka gudanar ranar 25 ga watan Fabrairun da ya gabata ba.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp