Gwamnan jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya Aminu Waziri Tambuwal, ya ce, sun kasa cimma matsaya kan ɗan takarar da za su marawa baya a tsakanin wata haɗaka ta mutum hudu da suka kafa domin daidaitawa wajen fitar da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.
Gwamnan ya ce a yanzu babu batun maslaha ko kuma wani ya janye wa wani a tsakanin masu neman takarar.
Gwamnan ya ce kafin wannan lokaci an yi tunanin tsakaninsa da Sanata Bukola Saraki da gwamnan Bauchi Bala Mohammad da Muhammad Hayatudeen da duk ke neman tikitin takara a inuwar PDP na iya maslaha a tsakaninsu.
Sai dai lura da yadda abubuwa ke tafiya kowa kawai tashi ta fisshe shi.