fidelitybank

Kou zama masu sanya idanu a bukukuwan Sallah – NSCDC

Date:

Hukumar tsaro ta NSCDC reshen jihar Jigawa, ta gargadi al’ummar jihar da su kasance masu lura da tsaro tare da kai rahoton duk wani motsi da suka samu a kusa da su musamman a lokacin bukukuwan ed-el Khabir.

Kwamandan NSCDC na jihar, Musa Alhaji Malah ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar CSC Adamu Shehu.

Ya ce rundunar ta tura jami’ai 1,125 domin samar da tsaro ga rayuka da dukiyoyin jama’a kafin bukin sallar Eid-el-Kabir, da kuma bayan bikin.

Kwamandan ya ce hakan ya yi daidai da umarnin kwamandan rundunar na samar da sa ido na tsawon sa’o’i 24 kan muhimman kadarorin kasa da ababen more rayuwa da kariya da kare rayukan fararen hula a fadin kasar nan.

A cewar sanarwar, “Kwamandan Musa Alhaji Malah (CC) ta hannun mataimakin kwamandan ayyuka DCC Kabiru Baffa ya ba da umarnin tura jami’ai da mazaje na musamman da sassa daban-daban na kananan hukumomi 27 na jihar nan take”.

Ya kuma umarci kwamandojin yankin, jami’an runduna, da kwamandojin sassan da su tabbatar da bin ka’idojin aiki.

Kwamandan, ya shawarci mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da ba jami’an tsaro hadin kai don yin bikin ba tare da wata matsala ba.

Ya kuma kara musu kwarin guiwa da su kai rahoto ga jami’an tsaro mafi kusa.

Kwamandan a madadin daukacin hafsoshi da jami’an rundunar, ya yi wa al’ummar Jigawa fatan gudanar da bukukuwan Sallah lafiya a gaba.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp