fidelitybank

Kotun ɗaukaka ƙara ta jingine hukuncinta a kan shari’ar Abba da Gawuna

Date:

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin, ta tanadi hukunci kan karar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar na kalubalantar tsige shi da kotun sauraron kararrakin zabe ta yi.

Ku tuna cewa kwamitin alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay ya kori Yusuf a ranar 20 ga Satumba, 2023.

Kotun ta bayyana kuri’u 165,663 na kuri’un Yusuf, saboda ba hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta sanya wa hannu ko tambari ba.

Sai dai a kotun daukaka kara a ranar Litinin, Wole Olanipekun, SAN, babban lauyan Yusuf, ya bukaci a yi watsi da hukuncin kotun.

Babban lauyan ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihi da wata kotu za ta soke zaben da aka yi kan rashin sanya hannu a bayan katin zabe.

Ya kara da cewa kotun ta yi kuskure, yana mai jaddada cewa wannan ne karo na farko da wata jam’iyyar siyasa za ta shigar da kara ba tare da shigar da dan takararta a matsayin jam’iyya ba kuma za a ayyana dan takarar a matsayin wanda ya lashe zaben.

Sai dai Lauyan jam’iyyar APC, Akin Olujimi, SAN, ya mayar da martani, inda ya ce kotunan daukaka kara ta bayyana karara cewa rashin sanya hannu kan kuri’u ya kasance na magudin zabe.

Kotun daukaka kara daga baya ta ajiye hukunci tare da sanar da cewa za a sanar da ranar ga bangarorin.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp