fidelitybank

Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Date:

Kotun Ƙolin Najeriya ta umarci babban akanta da babban bankin ƙasar wato CBN na Najeriya da su dakatar da kason kuɗin jihar Rivers, har sai gwamnan jihar ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban sahihan ƴan majalisar jihar.

Alƙalan kotun su biyar ne suka yanke wannan hukuncin, inda kotun ta ce Martins Amaewhule ne sahihin shugaban majajlisar.

Wannan ya kawo ƙarshen lokaci mai tsawo da aka ɗauka ana shari’a tsakanin ɓangarorin biyu kan rikita-rikitar siyasa a jihar.

Haka kuma ana ganin wannan matakin a matsayin wata nasara ga ɓangaren Ministan Abuja, Nyesome Wike, kan Gwamnan jihar, Sim Fubara.

Mai shari’a Emmanuel Agim ne ya karanta hukuncin, inda ya ce, “muna umartar Babban Bankin Najeriya CBN da Babban Akanta na Najeriya da su dakata da tura kuɗin kason jihar Rivers har sai gwamnan ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban majalisar jihar ƙarƙashin Martin Amaewhule,” kamar yadda ya bayyana.

A gefe guda kuma, a wata shari’ar daban, kotun ƙolin ta soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka yi a ranar 5 ga Oktoban 2024.

Mai shari’a Jamilu Tukur, ya ce zaɓen wanda hukumar zaɓen Rivers mai zaman kanta ta shirya, ya saɓa da sashe na 150 na kundin tsarin zaɓe na ƙasar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp