Wata babbar kotu a Zimbabwe ta hana bayar da kundin jerin sunayen masu zaɓe na kwamfuta bisa dalilai na tsaron ƙasa saboda zargin cewa za a iya yin maguɗi da zaɓe.
Kotun ta yanke wannan hukunci ne bayan da wani ɗan majalisar dokoki na hamayya Allan Makharm ya shigar da ƙara bayan da hukumar zaɓen ƙasar ta hana shi kwafin sunayen a watan Oktoba shekarar da ta wuce.
Ɗan majalisar ya nemi a ba shi sunayen a kwamfuta mai makon na takarda saboda a cewarsa na takardar nada yawa kuma zai yi masa tsada sosa ya yi fito da su.
A dangane da hakan ne babbar kotun Harare a jiya Talata ta yanke hukuncin cewa kundin sunayen muhimmin abu ne da ba za a baria fitar da shi ya bayyana ga jama’a ba ba tare da an yi la’akari da haɗarin sakin kundin ba ga tsaron ƙasa saboda za a iya yin maguɗi da shi.
A watan Yuli ne za a yi babban zaɓe a Zimbabwe.