fidelitybank

Kotun Legas ta ɗaure ɗan ƙasar Italiya

Date:

Kotun hukunta laifuka na musamman a Jihar Legas, ta ɗaure wata ‘yar ƙasar Italiya shekara uku a gidan yari saboda kama ta da laifin iƙirarin mallakar gidan da ba nata ba.

Mai Shari’a Mojisola Dada ta yanke hukuncin ne bayan ta kama matar mai suna Floriana De Stefani da laifi ɗaya cikin tuhuma shida da hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC ta gabatar a kanta, a cewar rahoton Channels TV.

Alƙaliyar ta ce matar ta gabatar da takardun boge wajen ikirarin mallakar gidan da take haya a cikinsa bayan mutuwar mijinta mai suna Luca Signorelli.

A ranar 30 ga watan Maris na 2019 ne EFCC ta gurfanar da ita a gaban kotun tare da wata ‘yar Najeriya, Stella Ogboru, tana tuhumar su da laifi biyar wanda daga baya aka mayar da su shida kuma aka cire sunan ‘yar Najeriyar.

An tuhume ta da amfani da takardun ƙarya, da satar kadara, laifukan da ta musanta waɗanda kuma suka sa aka shiga shari’ar.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp