Kotun duniya da ke birnin Hague ta yanke hukuncin cewa, dole ne kasar Rasha ta dakatar da mamaye kasar Ukraine cikin gaggawa.
Da kuri’u 13 zuwa biyu, mataimakin shugaban kasar Rasha Kirill Gevorgian na kasar Rasha da alkali Xue Hanqin na kasar Sin suka nuna rashin amincewarsu, kotun ICJ ta ce, Rasha za ta dakatar da ayyukan soji da ta fara a ranar 24 ga watan Fabrairu.
Hukuncin kotun wanda irin wannan hukunci na farko da kotun duniya ta yanke, tun bayan fara mamayar kasar Rasha.
Ya zama martani ne ga karar da kasar Ukraine ta shigar a ranar 27 ga watan Fabrairu, inda ta zargi Rasha da yin amfani da manufar kisan kiyashi, domin tabbatar da mamayar sojojinta.