Babbar Kotun Jihar Borno da ke zama a Maiduguri ta yanke wa Aisha Wakil, wadda aka fi sani da “Mama Boko Haram,” tare da wasu mutum biyu hukuncin shekaru 15 a gidan yari saboda zamba ta naira miliyan 6 a cikin cinikin mota.
Hukumar EFCC mai yaki da cin hanci da rashawa da kuma zagon kasa ga tattalin arzikin Najeriya ta bayyana hakan a ranar Litinin, tana mai cewa an yanke wa Aisha Wakil tare da Manajan Shirin ta na gidauniyar Complete Care and Aid Foundation, Tahiru Saidu Daura, da Daraktan Ƙasa, Lawal Shoyode, hukunci bayan an same su da laifin karɓar mota kirar Toyota Camry na shekarar 2012 daga wani mai ƙorafi ta hanyar zamba da ƙarya.
An sake gurfanar da su uku a watan Satumban 2020 kan tuhumar laifuka hudu da suka haɗa da haɗa kai, yaudara, da bayar da bayanan ƙarya, inda suka musanta aikata laifukan.
Bayan doguwar shari’a, Mai Shari’a Aisha Kumaliya ta yanke wa kowannen su hukuncin shekaru biyar a kurkuku a ranar Alhamis.