fidelitybank

Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Date:

Kotun Ƙolin Najeriya ta umarci babban akanta da babban bankin ƙasar wato CBN na Najeriya da su dakatar da kason kuɗin jihar Rivers, har sai gwamnan jihar ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban sahihan ƴan majalisar jihar.

Alƙalan kotun su biyar ne suka yanke wannan hukuncin, inda kotun ta ce Martins Amaewhule ne sahihin shugaban majajlisar.

Wannan ya kawo ƙarshen lokaci mai tsawo da aka ɗauka ana shari’a tsakanin ɓangarorin biyu kan rikita-rikitar siyasa a jihar.

Haka kuma ana ganin wannan matakin a matsayin wata nasara ga ɓangaren Ministan Abuja, Nyesome Wike, kan Gwamnan jihar, Sim Fubara.

Mai shari’a Emmanuel Agim ne ya karanta hukuncin, inda ya ce, “muna umartar Babban Bankin Najeriya CBN da Babban Akanta na Najeriya da su dakata da tura kuɗin kason jihar Rivers har sai gwamnan ya gabatar da kasafin kuɗin a gaban majalisar jihar ƙarƙashin Martin Amaewhule,” kamar yadda ya bayyana.

A gefe guda kuma, a wata shari’ar daban, kotun ƙolin ta soke zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka yi a ranar 5 ga Oktoban 2024.

Mai shari’a Jamilu Tukur, ya ce zaɓen wanda hukumar zaɓen Rivers mai zaman kanta ta shirya, ya saɓa da sashe na 150 na kundin tsarin zaɓe na ƙasar.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp