fidelitybank

Kotu za ta yanke hukuncin karshe tsakanin Fubara da APC

Date:

A yau Laraba ne kotun koli za ta yanke hukunci kan takaddamar da ake yi game da zaben gwamnan jihar Ribas.

Lamarin dai na tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP da Tonye Cole na jam’iyyar APC.

A makon da ya gabata ne alƙalai biyar na Kotun Koli karkashin jagorancin Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun suka saurari lauyoyin bangarorin biyu.

Bangarorin sun samu sanarwa daga babbar kotun cewa za a yanke hukuncin a ranar Laraba.

Cole yana kalubalantar nasarar Gwamna Fubara a zaɓen gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris na 2023 da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta gudanar a jihar.

A sakamakon zaɓen, Fubara ya samu kuri’u 302,614 inda ya doke abokin hamayyarsa, Tonye Cole wanda ya samu kuri’u 95,274.

Ganin haka ne ɗan takarar jam’iyyar APC ɗin ya ce an tafka maguɗi a zaɓen inda ya kuma ce Fubara bai cancanci tsayawa takarar ba saboda a lokacin yana kan muƙamin Akanta-Janar na jihar Ribas,kuma hakan ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar domin ya kamata ya fara yin murabus kafin tsayawa takara.

Bayan haka ne Cole ya kai maganar gaban kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamna inda ya nemi a tsige Fubara, amma aka yi watsi da ƙarar wanda hakan ya sa ya sake kai karar zuwa kotun ɗaukaka ƙara inda ita ma ta yi watsi da ƙarar tasa.

Ana sa ran kawo karshen takaddamar a hukuncin da kotun kolin za ta yanke a yau.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp