A yau Laraba ne kotun koli za ta yanke hukunci kan takaddamar da ake yi game da zaben gwamnan jihar Ribas.
Lamarin dai na tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP da Tonye Cole na jam’iyyar APC.
A makon da ya gabata ne alƙalai biyar na Kotun Koli karkashin jagorancin Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun suka saurari lauyoyin bangarorin biyu.
Bangarorin sun samu sanarwa daga babbar kotun cewa za a yanke hukuncin a ranar Laraba.
Cole yana kalubalantar nasarar Gwamna Fubara a zaɓen gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris na 2023 da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta gudanar a jihar.
A sakamakon zaɓen, Fubara ya samu kuri’u 302,614 inda ya doke abokin hamayyarsa, Tonye Cole wanda ya samu kuri’u 95,274.
Ganin haka ne ɗan takarar jam’iyyar APC ɗin ya ce an tafka maguɗi a zaɓen inda ya kuma ce Fubara bai cancanci tsayawa takarar ba saboda a lokacin yana kan muƙamin Akanta-Janar na jihar Ribas,kuma hakan ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar domin ya kamata ya fara yin murabus kafin tsayawa takara.
Bayan haka ne Cole ya kai maganar gaban kotun sauraron ƙararrakin zaɓen gwamna inda ya nemi a tsige Fubara, amma aka yi watsi da ƙarar wanda hakan ya sa ya sake kai karar zuwa kotun ɗaukaka ƙara inda ita ma ta yi watsi da ƙarar tasa.
Ana sa ran kawo karshen takaddamar a hukuncin da kotun kolin za ta yanke a yau.