fidelitybank

Kotu za ta yanke hukunci a kan wanda ya kashe dalibar makaranta a Kano

Date:

A ranar Alhamis ne ake sa ran wata babbar kotun jihar Kano, za ta yanke hukunci bisa kisan da aka yi wa wata karamar yarinya Hanifa Abubakar.

Ana zargin malaminta Abdulmalik Tanko  ne ya sace ta a watan Dasambar 2021 tare da kashe yarinyar mai shekara biyar, kana ya binne gawarta a gidansa.

Kisan nata ya ja hankalin duniya inda dubban mutane, ciki har da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, suka yi tur da shi.

Bayanai sun tabbatar da cewa wasu mutane ne suka ɗauke ta a babur mai kafa uku da ake kira A-Daidaita-Sahu bayan ta dawo daga makaranta a kan hanyarta ta zuwa gida inda suka tafi da ita.

An yi ta nema da cigiya amma sai bayan kwana 46 aka ji ɗuriyarta.

A watan Janairu ne aka gano gawar yarinyar da aka sace a ranar 4 ga watan Disambar 2021.

‘Yanda sanda sun tono gawarta tata wadda ake zargi Abdulmalik Tanko, mai makarantar  Noble Kids Academy, ya binne a wani rami.

An zarge shi da hada baki da Isyaku Hashim da matarsa Fatima Jibril da laifukan da suka hada da hada baki wajen aikata laifi, da satar mutum da kuma tsare yarinyar da suka sace ba tare da amincewarta ba da kuma kisan kai.

Sai dai kotu ta bayar da umarnin sakin Fatima Jibril bayan ta yi nasarar wanke kanta daga zarge-zargen a gaban kotu.

An kwashe kimanin watanni shida ana shari’ar wadda Mai Shari’a Sulaiman Na’abba yake jagoranta. In ji BBC.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp