Kotun ƙoli ta ce nan gaba ne za ta sanar da za ta yanke hukunci kan arar da aka ɗaukaka kan zaɓen gwamna na jihar Ebonyi.
Alƙali John Okoro ya ɗauki matakin ne bayan da ɓangarorin da ke shari’ar suka amince da jawaban da suka yi gaban kotun.
Kotun ɗaukaka ƙara a jihar Legas tun farko ta tabbatar da Francis Nwifuru a matsayin halastaccen gwamnan jihar Ebonyi.
Alƙalan shari’ar ƙarƙashin jagorancin Jummai Sankey ya kori ƙarar da Chukwuma Odii na Jam’iyyar PDP ya shigar.
Tawagar alƙalan ta kori duka batutuwa biyar da wanda ya shigar da ƙarar ya yi tare da korar ƙarar saboda rashin ƙwararan hujjoji.
Mai shari’a Jummai Sankey ta ce PDP da ɗan takararta ba su da hurumin shiga harkokin da suka shafi APC dangane da batun tsayar da dan takara.