fidelitybank

Kotu za ta sake nazari akan zargin da ake wa mawakin da ya mutu na lalata da yara

Date:

Wata kotu a Amurka ta ce, za ta sake nazarin zargin cin zarafin lalata da ƙananan yara da wasu mutum biyu ke yi wa shahararren mawaƙin nan ɗan ƙasar Amurka – da ya rasu – Michael Jackson.

Mutanen biyu – waɗanda a yanzu shekarunsu 40 – sun shigar da ƙarar kamfanin mawaƙin, inda suke zargin Michael Jackson da cin zarafinsu ta hanyar lalata a lokacin da suke ƙananan yara.

Wade Robson da James Safechuck, a yanzu kotu za ta saurari ƙarar da a baya wata kotu ta yi watsi da ita.

Mutanen biyu sun ce haƙƙin kamfanonin mawaƙin ne su kare su a lokacin da abin ya faru.

Lauyoyin Michael – wanda ya rasu a shekarar 2009 – sun ce bai aikata laifin ba.

Rabson da Safechuck sun zargi Michael Jackson da cin zarafinsu a shekarun 1980 da 1990 a lokacin da suke zaune a gidan gonarsa da ke Neverland.

An bayyana zargin a cikin wani film da aka yi kan rayuwarsa a 20019 mai suna ‘Leaving Neverland’, fim ɗin da iyalan Micheal suka bayyana da ɓata-sunan marigayin

A shekarar 2020, alƙalin kotun Los Angeles ya yanke hukuncin cewa mista Safechuck ba shi da ikon shigar da kamfanonin Jackson ƙara, yana mai kafa hujja da cewa kamfanonin ba su da hurumin kula da kariyarsa.

A 2012 kuma alƙalin ya zartar da irin wannan hukunci kan Mista Robson saboda irin waɗannan hujojoji.

To sai dai a ranar Juma’a wata kotun ɗaukaka ƙara a California ta warware hukuncin na baya, tana mai cewa dole ne kamfanin na sauke nauyin da ke kansa na kare haƙƙin ƙananan yara.

“Ba zai yiwu a ƙyale kamfani ya riƙa dillancin lalata ƙananan yara ba, don kawai mamallakin kamfanin ake zargi da aikata laifin”, in ji kotun.

Ta ƙara da cewa ”sakaci ne kamfanin ya ɗauka ba shi da haƙƙin kare ƙananan yara, don haka wannan kotu za ta sake nazarin wannan sharia’a domin yiyuwar tuhumar kamfanonin”.

Lauyan mutanen biyu, Vince Finaldi, ya ce kotu ta yi watsi da hukuncin farko wanda ya saɓa wa dokokin Carlifornia.

A nasa ɓangare, lauyan Micheal Jackson, Jonathan Steinsapir, ya ce yana da yaƙinin cewa wanda yake karewa bai aikata laifin ba.

Ya ci gaba da cewa duka zarge-zargen sun saɓa wa ƙwararan hujjojin da suke da su. In ji BBC.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp