fidelitybank

Kotu za ta sake nazari akan zargin da ake wa mawakin da ya mutu na lalata da yara

Date:

Wata kotu a Amurka ta ce, za ta sake nazarin zargin cin zarafin lalata da ƙananan yara da wasu mutum biyu ke yi wa shahararren mawaƙin nan ɗan ƙasar Amurka – da ya rasu – Michael Jackson.

Mutanen biyu – waɗanda a yanzu shekarunsu 40 – sun shigar da ƙarar kamfanin mawaƙin, inda suke zargin Michael Jackson da cin zarafinsu ta hanyar lalata a lokacin da suke ƙananan yara.

Wade Robson da James Safechuck, a yanzu kotu za ta saurari ƙarar da a baya wata kotu ta yi watsi da ita.

Mutanen biyu sun ce haƙƙin kamfanonin mawaƙin ne su kare su a lokacin da abin ya faru.

Lauyoyin Michael – wanda ya rasu a shekarar 2009 – sun ce bai aikata laifin ba.

Rabson da Safechuck sun zargi Michael Jackson da cin zarafinsu a shekarun 1980 da 1990 a lokacin da suke zaune a gidan gonarsa da ke Neverland.

An bayyana zargin a cikin wani film da aka yi kan rayuwarsa a 20019 mai suna ‘Leaving Neverland’, fim ɗin da iyalan Micheal suka bayyana da ɓata-sunan marigayin

A shekarar 2020, alƙalin kotun Los Angeles ya yanke hukuncin cewa mista Safechuck ba shi da ikon shigar da kamfanonin Jackson ƙara, yana mai kafa hujja da cewa kamfanonin ba su da hurumin kula da kariyarsa.

A 2012 kuma alƙalin ya zartar da irin wannan hukunci kan Mista Robson saboda irin waɗannan hujojoji.

To sai dai a ranar Juma’a wata kotun ɗaukaka ƙara a California ta warware hukuncin na baya, tana mai cewa dole ne kamfanin na sauke nauyin da ke kansa na kare haƙƙin ƙananan yara.

“Ba zai yiwu a ƙyale kamfani ya riƙa dillancin lalata ƙananan yara ba, don kawai mamallakin kamfanin ake zargi da aikata laifin”, in ji kotun.

Ta ƙara da cewa ”sakaci ne kamfanin ya ɗauka ba shi da haƙƙin kare ƙananan yara, don haka wannan kotu za ta sake nazarin wannan sharia’a domin yiyuwar tuhumar kamfanonin”.

Lauyan mutanen biyu, Vince Finaldi, ya ce kotu ta yi watsi da hukuncin farko wanda ya saɓa wa dokokin Carlifornia.

A nasa ɓangare, lauyan Micheal Jackson, Jonathan Steinsapir, ya ce yana da yaƙinin cewa wanda yake karewa bai aikata laifin ba.

Ya ci gaba da cewa duka zarge-zargen sun saɓa wa ƙwararan hujjojin da suke da su. In ji BBC.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp